DCL Hausa Radio
Kaitsaye

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

-

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a duk faɗin ƙasar.

INEC ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba, 30 ga Yuli, inda ta bayyana cewa aikin rijistar zai gudana daga matakin jihohi zuwa kananan hukumomi a fadin Najeriya.

Google search engine

Hukumar ta kuma yi gargadi ga ‘yan Najeriya da ke yawan yin rajista fiye da ɗaya, da kuma wadanda shekarunsu bai kai na rajista ba, da su guji karya doka, tana mai cewa za ta yi amfani da sabbin hanyoyin zamani don gano masu karya doka don fuskantar hukunci.

INEC ta ce ta shirya tsaf wajen gudanar da aikin cikin gaskiya da bin ka’ida, tare da tabbatar da cewa kowane ɗan ƙasa ya samu damar yin rajista cikin sauƙi da adalci kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnonin da suka sha suka ta yanzu sun koma jam’iyyar APC – Ministan Abuja Wike

Ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce ficewar wasu gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyyar APC ta tabbatar da goyon bayansa ga Shugaba...

Majalisar Dattawan Nijeriya za ta tantance sabon shugaban INEC ranar Alhamis

Majalisar Dattawan Nijeriya ta shirya tantance Farfesa Joash Amupitan, wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya zaba domin zama sabon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, a...

Mafi Shahara