DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dattawan Nijeriya ta ba shugaban NNPCL wa’adin mako 3 bayyana kan batan Naira tiriliyan 210

-

Majalisar dattawan Najeriya ta bai wa Shugaban kamfanin man fetur na kasa (NNPCL), Bayo Ojulari, wa’adin makonni uku domin ya bayyana cikakken bayani kan inda aka karkatar da Naira tiriliyan 210 daga shekarar 2017 zuwa 2023.

Sanata Ahmed Wadada, shugaban kwamitin Majalisar kan lissafin kuɗin jama’a, ne ya bayyana hakan bayan zaman tattaunawa da Ojulari ranar Talata.

Google search engine

Wadada ya ce ba wai an sace kudaden ba ne, ko kuma sun bace, sai dai babu cikakken bayani kan yadda aka kashe su, wanda hakan ya haifar da cece-kuce daga ‘yan Majalisa da masu ruwa da tsaki a tattalin arzikin ƙasar.

Majalisar ta bukaci Ojulari ya gabatar da cikakken bayani kan dukkan tuhumar da ke cikin rahoton binciken nan da makonni uku.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara