Tsohon Sanatan da ya wakilci yankin Kogi ta Yamma, Dino Melaye, ya sanar da murabus dinsa daga jam’iyyar PDP mai adawa a Nijeriya, yana mai zargin jam’iyyar da rashin iya jagoranci nagari da gaza kawo sauyi ga rayuwar ‘yan Nijeriya.
A cikin wasikar murabus da ya wallafa a shafinsa na X ranar Alhamis, mai dauke da kwanan wata 4 ga Yuli, 2025, kuma aka aika zuwa ga shugaban PDP na mazabar Ward 1, Aiyetoro Gbede, karamar hukumar Ijumu a jihar Kogi, Melaye ya bayyana cewa ya fice gaba daya daga dukkan harkokin jam’iyyar nan take.
Melaye, wanda ya tsaya takarar gwamnan Jihar Kogi a ƙarƙashin jam’iyyar PDP a zaben 2023, ya bayyana cewa matakin da ya ɗauka ya biyo bayan zurfin tunani ne game da halin da jam’iyyar ke ciki da kuma inda take nufa a gaba.



