Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta karɓi ‘yan ƙasar 139 da suka dawo daga Agadez, Jamhuriyar Nijar, a ci gaba da kokarinta na dawo da ‘yan Nijeriya da suka makale a wasu kasashen.
Wadanda suka dawo sun iso filin jirgin sama na Malam Aminu Kano da ke Kano da yammacin ranar Talata, 29 ga Yuli, 2025, ta jirgin Sky Mali da ya sauka misalin ƙarfe 7:57 na dare.
A cewar ofishin NEMA na jihar Kano da ya fitar da bayani a shafinsa na X ranar Alhamis, waɗanda suka iso sun haɗa da manya maza 22, manya mata 52, yara maza 33 da kuma yara mata 32.



