DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumomi a Nijeriya sun karbi ‘yan kasar 139 daga jamhuriyar Nijar

-

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta karɓi ‘yan ƙasar 139 da suka dawo daga Agadez, Jamhuriyar Nijar, a ci gaba da kokarinta na dawo da ‘yan Nijeriya da suka makale a wasu kasashen.

Wadanda suka dawo sun iso filin jirgin sama na Malam Aminu Kano da ke Kano da yammacin ranar Talata, 29 ga Yuli, 2025, ta jirgin Sky Mali da ya sauka misalin ƙarfe 7:57 na dare.

Google search engine

A cewar ofishin NEMA na jihar Kano da ya fitar da bayani a shafinsa na X ranar Alhamis, waɗanda suka iso sun haɗa da manya maza 22, manya mata 52, yara maza 33 da kuma yara mata 32.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara