DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ma’aikatan lafiya da ungozomomi a Nijeriya sun janye yajin aikin da suka shiga – In ji Ministan Lafiya

-

Kungiyar ma’aikatan jinya da ungozoma ta Nijeriya ta janye yajin aikin da ta fara, kamar yadda ministan lafiya, Farfesa Ali Pate ya tabbatar a yau Juma’a bayan wani taron sirri da shugabannin kungiyar.

Ministan ya bayyana wa manema labarai cewa an cimma matsaya tsakanin gwamnati da shugabannin kungiyar, wanda hakan ne ya sa aka dakatar da yajin aikin.

Sai dai shugabannin kungiyar ta ki yin wani bayani ga manema labarai bayan kammala taron.

Tun ranar 29 ga watan Yuli, 2025 ne kungiyar NANNM ta fara yajin aikin gargadi na mako guda saboda kin daukar mataki daga gwamnatin tarayya, bayan kungiyar ta mika wa gwamnati gargaɗi na kwanaki 15 tun daga 14 ga Yuli, 2025.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara