Ɗaya daga cikin wadanda suka kafa jam’iyyar PDP, Farfesa Jerry Gana, ya bayyana cewa Peter Obi zai kayar da kowane dan takara a jihohin Arewa matukar ya tsaya takara a karkashin jam’iyyar PDP.
Yayin wata hira da yayi a Arise TV, Farfesa Gana ya ce binciken ra’ayoyin jama’a da ya gudanar ya nuna cewa mutanen Arewa masu adalci ne, kuma suna ganin Peter Obi a matsayin dan takara mai gaskiya da nagarta.
A shekara ta 2022, Peter Obi ya bar jam’iyyar PDP domin tsayawa takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar Labour Party, inda ya yi fice sosai a zaben 2023.
Farfesa Gana ya kuma tunatar da ’yan Najeriya cewa jam’iyyar PDP ta kafa turba mai kyau tun daga lokacin da ta taimaka wajen dawo da mulkin dimokuradiyya a 1999.


