Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na Nijeriya Mohammed Idris, ya bayyana cewa hukumar kula da kafafen yada labarai ta kasa NBC ce kadai ke da ikon janye lasisin kowanne gidan rediyo ko talabijin ba gwamnoni ba.
Ministan ya bayyana hakan ne a wani martani kan matakin da gwamnan jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya dauka na rufe Gidan Rediyon Badeggi FM da kuma umarnin a kwace lasisin aikinsa, bisa zargin yada shirye-shiryen da ke tunzura jama’a da saba ka’idojin aiki.
Matakin ya haifar da cece-kuce da suka daga sassa daban-daban, ciki har da Amnesty International, wadda ta soki gwamnatin jihar bisa tuhumar ta da take hakkin ‘yancin kafafen yada labarai.
Ministan ya bayyana cewa, a tsarin doka, ba wani gwamna ko jami’in gwamnati da ke da ikon rufe kafar yada labarai kai tsaye ko kwace lasisinta.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Ministan ya nuna damuwa kan korafe-korafen da gwamnatin ta gabatar dangane da rufe gidan rediyon Badeggi FM.
Ya tabbatar da cewa za a warware lamarin cikin gaskiya da adalci, tare da bin doka da ka’idojin da hukumar da ke kula da gidajen rediyo da talabijin (NBC) ta shimfida.



