DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar Amnesty International ta caccaki gwamnatin Nijeriya kan shiru, bayan shekara 6 da batan Dadiyata

-

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta soki gwamnatin Nijeriya kan yadda ta ci gaba da yin shiru tsawon shekara shida bayan bacewar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata, ba tare da wani bayani ko bincike mai ma’ana ba.

Dadiyata, wanda malami ne a Sashen Harsuna na Jami’ar Tarayya Dutsinma, kuma fitaccen mai sharhi a kafafen sada zumunta daga jihar Kaduna, ya bace ne tun ranar 2 ga Agusta, 2019, bayan wasu da ba a san ko su wanene ba sun tafi da shi daga gidansa da misalin ƙarfe 1 na dare.

A wani taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna ranar Asabar, Isa Sanusi, Daraktan Amnesty International a Nijeriya, ya bayyana cewa rashin jajircewar gwamnati wajen gano inda Dadiyata yake ko binciken lamarin ya kara nuna hadarin da masu sukar gwamnati ke fuskanta a kasar.

Sanusi ya kara da cewa wannan lamari yana nuni da irin halin matsin lamba da ‘yan Nijeriya ke ciki wajen bayyana ra’ayoyinsu cikin ‘yanci, yana mai kira ga gwamnati da ta dauki mataki gaggawa domin fayyace gaskiyar lamarin tare da kare hakkin dan Adam a kasar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara