Kungiyar ma’aikatan jinya da ungozomomin Nijeriya ta dakatar da yajin aikin gargadi na kwana bakwai da ta fara a fadin ƙasa.
Mataimakin Sakataren Janar na ƙungiyar, Chidi Aligwe, ne ya bayyana hakan ga jaridar Punch a yau Asabar.
A ranar Laraba ne ma’aikatan jinya da unguwanni suka fara yajin aikin gargadi na mako guda domin matsa lamba kan buƙatun da suka dade suna nema, wanda suka haɗa da ƙarin kuɗin aiki da dare, daidaita kudin kayan aik, ware tsarin albashi na musamman ga ma’aikatan jinya, ƙarin kuɗin aiki na musamman, ɗaukar sabbin ma’aikatan jinya da kuma sashen kula da harkokin jinya a cikin ma’aikatar lafiya ta kasa.
An dakatar da yajin aikin ne a ranar Asabar bayan wani taron gaggawa ta hanyar yanar gizo da shugabannin ƙasa na ƙungiyar suka gudanar.


