DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ma’aikatan lafiya a Nijeriya sun janye yajin aikin da suka shiga

-

Kungiyar ma’aikatan jinya da ungozomomin Nijeriya ta dakatar da yajin aikin gargadi na kwana bakwai da ta fara a fadin ƙasa.

Mataimakin Sakataren Janar na ƙungiyar, Chidi Aligwe, ne ya bayyana hakan ga jaridar Punch a yau Asabar.

A ranar Laraba ne ma’aikatan jinya da unguwanni suka fara yajin aikin gargadi na mako guda domin matsa lamba kan buƙatun da suka dade suna nema, wanda suka haɗa da ƙarin kuɗin aiki da dare, daidaita kudin kayan aik, ware tsarin albashi na musamman ga ma’aikatan jinya, ƙarin kuɗin aiki na musamman, ɗaukar sabbin ma’aikatan jinya da kuma sashen kula da harkokin jinya a cikin ma’aikatar lafiya ta kasa.

An dakatar da yajin aikin ne a ranar Asabar bayan wani taron gaggawa ta hanyar yanar gizo da shugabannin ƙasa na ƙungiyar suka gudanar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara