Tsohon dan majalisar dattawa Dino Melaye, ya bayyana cewa matsin tattalin arziki da yunwa a Nijeriya na kara muni, yana mai cewa mutane da dama sun kasa samun abincin da za su ci kullum.
A wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels TV ranar Juma’a, Melaye ya ce halin da ‘yan Najeriya ke ciki karkashin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu bai taɓa faruwa ba a baya.
Melaye, wanda ya wakilci mazabar Kogi ta Yamma, ya bayyana cewa gwamnatin APC ba ta iya jagoranci ba domin har yanzu ta kasa sanya kwanciyar hankali ko nemo mafita ga matsalolin kasar.


