DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Abuja ba za ta gyaru cikin shekaru biyu ba – Minista Wike

-

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya bayyana cewa ba zai yiwu a kawo sauyi a dukkanin fannonin ci gaban Abuja cikin shekaru biyu kacal ba, yana mai cewa hakan ba shi da tushe a zahiri.

Wike ya bayyana hakan ne a lokacin wani taron tattaunawa da manema labarai da aka gudanar a Abuja a ranar Litinin, inda ya mayar da martani kan korafe-korafen da suka shafi gibin da ake samu a bangaren gine-gine, ilimi, lafiya da sufuri.

Ya bukaci ‘yan Najeriya da su fahimci cewa gudanar da gwamnati na bukatar lokaci da tsara abubuwa bisa fifiko.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara