DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya bai wa kowacce ‘yar wasan D’Tigress dala 100,000

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bai wa kowacce ‘yar wasan ƙungiyar kwallon kwando ta mata ta D’Tigress, kyautar dala 100,000 bayan nasarar da suka samu a gasar AfroBasket.

An sanar da hakan ne a wani taron tarbar nasara da aka shirya a fadar shugaban kasa a ranar Litinin, inda mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya wakilci Shugaban Ƙasa a wajen bikin.

Google search engine

Shugaban ya yaba da bajintar ‘yan wasan da suka sanya sunan Nijeriya a mataki na duniya, tare da nuna cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa wasanni, musamman ma mata.

Matar shugaban kasa Oluremi Tinubu, shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa Femi Gbajabiamila, da wasu jami’ai ne suka tarbi tawagar D’Tigress da mai horaswa Rena Wakama.

D’Tigress ta doke Mali da ci 78–64 a wasan ƙarshe da aka buga a kasar Côte d’Ivoire ranar Lahadi, inda suka lashe kofin kwallon kwandon mata na Afrika wato AfroBasket karo na bakwai kuma karo na biyar a jere.

Wannan karramawar ta zo ne mako guda bayan da Shugaba Tinubu ya karrama ƙungiyar Super Falcons da dala 100,000 kowacce, bayan nasarar lashe gasar WAFCON karo na 10 a Morocco, abin da ya jawo ce-ce-ku-ce da martani daga ‘yan Najeriya a kafafen sada zumunta.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara