DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Har yanzu gigin hana El-Rufai muƙamin minista bai sake shi ba – Martanin APC ga kalaman El’rufai

-

Jam’iyyar APC ta soki kalaman tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, inda ta ce cike suke da rashin gaskiya da ruɗani.

Felix Morka, mai magana da yawun jam’iyyar, ya bayyana hakan a wata sanarwa, yana mai cewa El-Rufai na ci gaba da nuna bacin ransa kan gazawarsa ta zama minista, yana amfani da harshen batanci domin ɓata wa gwamnatin Tinubu suna.

Google search engine

Jigon a jam’iyyar haɗaka ta ADC ya ce sake zaben Shugaba Tinubu tamkar rushe sauran haɗin kan Nijeriya ne.

A cewar APC, El-Rufai da abokan tafiyarsa a jam’iyyar ADC ba su da wata manufa sai girman kai da kishin kansu, kuma ba su da wata hanya ko shiri da zai fi nasarorin da gwamnatin Tinubu ke samu a yanzu, kamar yadda ake gani a fannin noma, wutar lantarki, fitar danyen mai, gina hanyoyi, sauƙin hauhawar farashi da tallafin karatu na NELFUND.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara