Hukumar shirya jarabawar kammala sakandire ta yammacin Afirka (WAEC) ta fitar da sakamakon jarabawar WASSCE na shekarar 2025, inda aka samu gagarumar faduwar dalibai.
Daga cikin dalibai 1,969,313 da suka zauna jarabawar, dubu 754,545 ne kawai suka samu maki mai kyau aƙalla a darussa 5 da suka haɗa da Turanci da Lissafi, wanda ke nuni da kashi 38.32 cikin 100 ne kacal suka samu nasarar.
Shugaban ofishin WAEC a Najeriya, Amos Dangut, ya bayyana cewa an samu raguwa da kashi 33.8% idan aka kwatanta da sakamakon daliban da suka zauna jarrabawar a shekarun baya.




Da fatan kuna lafiya, gaskiya sakamakon jarabawa daga jamb zuwa waec na bana ya kara tabbatar da tabarbarewar harkar ilimi a Nigeria, musamman bangaren makarantun gwamnati, la’akari da masu fadiwa ta bangaren su, hakan kuma yana nuni kan ana so a gigita makarantun kudi na yaya masu hanu da shuni ne, a bar ya’yan talakawa kara zube ta bangaren ilimi sai dai muce Allah ya kyauta, ina godiya ku huta lafiya daga naku mai sauraron ku ya da kullum Ayuba Aufu Michika