DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilai ta bukaci a bude iyakokin tudu na Nijeriya 

-

By Salamatu Alhassan Musa

Kwamitin majalisar wakilai kan harkokin hukumar hana fasa kwauri ta Nijeriya da haraji ya bayyana damuwa kan ci gaba da rufe wasu iyakokin ƙasar.

Google search engine

Shugaban kwamitin, Leke Abejide, ya ce ci gaba da rufe iyakokin ba ya amfani ga tattalin arzikin ƙasar, inda ya bayyana cewa Nijeriya na asarar kuɗaɗen shiga masu yawa sakamakon wannan rufewar.

Ya yi wannan bayani ne a Kaduna yayin da ya jagoranci wasu daga cikin mambobin kwamitin a ziyarar gani da ido a Yankin Zone B na hukumar Kwastan ta Nijeriya, da ya ƙunshi jihohin Kano, Jigawa, Katsina, Sokoto, Zamfara, Kebbi, Neja, Kogi, Kwara da kuma Birnin Tarayya Abuja.

Abejide, wanda ya kuma tabo bukatar haɗin gwiwar jami’an tsaro domin dakile matsalar rashin tsaro da ke ƙara shafar samun kuɗaɗen shiga a yankin, inda ya ce kwamitin zai ɗauki matakin gabatar da kudiri a zauren majalisa bayan komawarsu daga hutu na shekara.

Ya ce kudirin zai kasance tare da haɗin gwiwar sauran kwamitocin da ke da alaka da harkokin tsaro, tare da yiwuwar haɗa hannu da takwarorinsu na majalisar dattawa, domin nemo mafita ta dindindin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

El-Rufa’i ya kai karar kwamishinan ‘yan sandan jihar Kaduna kan zargin rashin kwarewar aiki

Tsohon gwamnan Kaduna Malam Nasiru El-rufa'i ya shigar da karar kwamishinan 'yan sandan jihar gaban hukumar 'yan sanda ta kasa bisa zargin rashin kwarewa da...

Za mu taka wa yawan ciyo basuka a Nijeriya birki – Tajuddeen Abbas

Kakakin majalisar wakilai Tajuddeen Abbas ya nuna damuwa da yawan ciyo basuka da ake yi a Najeriya, yana mai bayyana hakan a matsayin lamarin da...

Mafi Shahara