DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jonathan ne dantakara mafi nagartar da zai tsaya wa PDP takara a zaben 2027 – Sule Lamido

-

 

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya bayyana tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan a matsayin mafi ƙarfi da dacewa da zama ɗan takarar shugabancin ƙasa na jam’iyyar PDP a zaɓen 2027, yana mai kira ga jam’iyyar ta yi ƙoƙarin dawo da shi.

Google search engine

Rahoton gidan talabijin na Channels ya ambato Sule Lamido na buga misalin yadda Jonathan ya shugabanci Nijeriya cikin kwarewa da iya mulki, kuma yana iya aiki da kowa.

Ya ƙara da cewa babu wani ɗan jam’iyyar daga Kudanci a yanzu da zai iya kaiwa matakin gogewar Jonathan da zai samu tikitin takara a jam’iyyarsu ta PDP.

Ya jaddada cewa idan PDP za ta bai wa Kudanci takarar shugabancin ƙasa, babu wanda zai iya fafatawa da Jonathan wajen cancanta, gogewa, da iya sauraron ra’ayoyin jama’a.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara