DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsohon ministan noma a Nijeriya Cif Audu Ogbeh ya rasu yana da shekaru 78 a duniya

-

Tsohon Ministan Noma da Cigaban Karkara, Cif Audu Ogbeh, ya rasu a ranar Asabar, 9 ga Agusta 2025, yana da shekaru 78 a Duniya.

A wata sanarwa da iyalansa suka fitar, sun bayyana cewa marigayin ya rasu ba tare da wata jinya ba, ya kuma bar tarihin gaskiya, rikon amana, da sadaukarwa ga ƙasa da al’umma. Sun ce Ogbeh ya shafe rayuwarsa yana bautawa ƙasa da bayar da gudummawa mai muhimmanci ga ci gaban al’umma.

Google search engine

Jaridar Punch ta ambato iyalan mamacin na godiya ga duk masu yi musu ta’aziyya, tare da sanar da cewa za a bayyana cikakkun shirye-shiryen jana’iza a nan gaba. Sun kuma roƙi a basu damar yin jimami cikin sirri a wannan lokaci na rashin makusanci da aka yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi da karin girma na malaman jami’o’i

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta saki kudin da ya kai Naira biliyan 2.3 domin biyan bashin albashi da karin girma na malamai a jami’o’in...

Majalisar wakilan Nijeriya ta amince wa Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.35

Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban Tinubu na neman bashin dala biliyan 2.347 daga ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025...

Mafi Shahara