DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Uwargidar shugaban Nijeriya ta ba da tallafin naira miliyan 110 ga iyalan ‘yan wasan Kano da suka rasu a hatsari

-

Uwargidar shugaban ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta bayar da tallafin Naira miliyan 110 ga iyalan ‘yan wasan Kano 22 da suka rasu a mummunan hatsarin mota a watan Mayu.

Rahoton gidan talabijin na Channels ya ce kowane iyali ya samu Naira miliyan 5 ta hannun Victim Support Fund, wani shiri na gwamnati da ke taimaka wa waɗanda suka shiga cikin bala’i da matsanancin hali.

Google search engine

Fadar shugaban ƙasa ta ce wannan taimako na cikin shirin gidauniyar Renewed Hope na shugaban ƙasa Bola Tinubu, tare da nuna tausayawa da kulawa daga tsagin jagoranci.

‘Yan wasan sun rasu ne a kan hanyar Kano–Kaduna yayin dawowa daga gasar National Sports Festival a jihar Ogun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaban Amurka Donald Trumph ya haramtawa Farfesa Wole Soyinka zuwa kasar

Gwamnatin Amurka karkashin jagorancin shugaba Donald Trump ta soke takardar izinin shiga ƙasar ga Farfesa Wole Soyinka, sanannen marubuci a duniya. Farfesa Soyinka ya bayyana hakan...

Hukumar agajin gaggawa NEMA ta karɓi ƴan Nijeriya 153 da suka makale a Chadi

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA, ta bayyana cewa ta karɓi ’yan Nijeriya 153 da suka dawo daga ƙasar Chadi, ƙarƙashin shirin Ƙungiyar...

Mafi Shahara