DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Atiku ya jinkirta yankar katin ADC, bayan rade-radin zawarcin Jonathan da aka ce jam’iyyar na yi

-

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya dakatar da shirin karbar katin zama mamba na jam’iyyar ADC, yayin da ake rade-radin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan na iya shiga takarar shugaban kasa a 2027 tare da neman goyon bayan jam’iyyar.

Atiku, wanda ya fice daga PDP bayan rikice-rikicen cikin gida, ya shirya karbar katin a mazabarsa ta Jada, Adamawa, a ranar 6 ga Agusta, amma an dage taron ba tare da saka sabon lokaci ba.

Google search engine

Shugaban ADC na Adamawa, Shehu Yohana, ya ce Atiku na jiran wasu gwamnoni daga APC su koma ADC kafin a gudanar da muhimmin taron.

Sai dai jaridar Punch ta ce wasu jiga-jigan ADC sun nuna jinkirin na iya zama saboda takaddama tsakanin Atiku da tsohon dan takarar shugaban kasa na LP, Peter Obi, wanda ake zargin ya mamaye tsarin jam’iyyar a Kudu.

Sun kuma yi hasashen cewa idan lamarin bai tafi yadda Atiku ke so ba, zai iya komawa jam’iyyar SDP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara