DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Atiku ya jinkirta yankar katin ADC, bayan rade-radin zawarcin Jonathan da aka ce jam’iyyar na yi

-

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya dakatar da shirin karbar katin zama mamba na jam’iyyar ADC, yayin da ake rade-radin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan na iya shiga takarar shugaban kasa a 2027 tare da neman goyon bayan jam’iyyar.

Atiku, wanda ya fice daga PDP bayan rikice-rikicen cikin gida, ya shirya karbar katin a mazabarsa ta Jada, Adamawa, a ranar 6 ga Agusta, amma an dage taron ba tare da saka sabon lokaci ba.

Google search engine

Shugaban ADC na Adamawa, Shehu Yohana, ya ce Atiku na jiran wasu gwamnoni daga APC su koma ADC kafin a gudanar da muhimmin taron.

Sai dai jaridar Punch ta ce wasu jiga-jigan ADC sun nuna jinkirin na iya zama saboda takaddama tsakanin Atiku da tsohon dan takarar shugaban kasa na LP, Peter Obi, wanda ake zargin ya mamaye tsarin jam’iyyar a Kudu.

Sun kuma yi hasashen cewa idan lamarin bai tafi yadda Atiku ke so ba, zai iya komawa jam’iyyar SDP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnonin da suka sha suka ta yanzu sun koma jam’iyyar APC – Ministan Abuja Wike

Ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce ficewar wasu gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyyar APC ta tabbatar da goyon bayansa ga Shugaba...

Majalisar Dattawan Nijeriya za ta tantance sabon shugaban INEC ranar Alhamis

Majalisar Dattawan Nijeriya ta shirya tantance Farfesa Joash Amupitan, wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya zaba domin zama sabon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, a...

Mafi Shahara