DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa

-

An yi imanin cewa tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi murabus daga mukaminsa saboda dalilai uku da suka shafi rikicin siyasa da matsin lamba daga bangarori daban-daban.

Majiyoyi sun bayyana wa jaridar Daily Trust cewa, dalili na farko shi ne kokarin janyo tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, cikin jam’iyyar APC, inda aka bukaci Ganduje da ya hakura da mukaminsa tare da alkawarin samun wani babban matsayi a gaba.

Google search engine

Dalili na biyu kuwa ya shafi rade-radin samun sabani tsakaninsa da fadar shugaban kasa, wanda ya haifar da matsin lamba da ya sa ya sauka daga mukaminsa.

Dalili na uku kuma shi ne bukatar kwantar da hankalin ƴan yankin Arewa ta Tsakiya, waɗanda ke neman rike wannan kujera tun bayan saukar tsohon shugaban jam’iyyar, Abdullahi Adamu.

Wata majiya ta kusa da Ganduje ta ce matsalarsa ta fara ne lokacin da aka umarce shi ya yi sasanci da tsohon ubangidansa kuma abokin adawarsa a siyasa, Rabiu Musa Kwankwaso — wanda rikicin siyasa tsakaninsu ya yi tsanani a baya.

Duk da rashin jin dadin wannan mataki, an ce Ganduje ya yi kokarin shawo kan lamarin, yana fatan daga baya zai iya jawo hankalin shugaban kasa zuwa gare shi.

Rahotanni sun kuma nuna cewa fadar shugaban kasa na ganin Kwankwaso ne ke da tasiri da mafi rinjaye a Kano, wanda zai iya taimakawa jam’iyyar a zaben 2027.

Sai dai rashin jituwa tsakaninsa da Ganduje na iya zama cikas ga shigar Kwankwaso cikin jam’iyyar, tare da yiwuwar haifar da sabbin rikice-rikice kan jagorancin APC a jihar.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara