Sabbin bayanai na nuni da cewa an kai hare-hare a kauyuka 15 da ke jihar Zamfara, tsakanin ranakun 4 zuwa 10 ga watan Agustan 2025.
A wani rahoto da kungiyar Zamfara Circle Community Initiative ta fitar, hare-haren sun kai ga yin garkuwa da mutane 144, da kashe wasu 24, tare da jikkata wasu mutane 16 a wasu kananan hukumomi da dama.
Al’umomin da abin ya shafa sun hada da Sabe, Tungar Yamma, Sauru, Lambasu, Dogon Madacci, Dankalgo, da Kwanar Kalgo a karamar hukumar Bakura.
A karamar hukumar Tsafe, an kai hare-haren a Chediya, Kucheri, Yankuzo, da Katangar Gabas Bilbils.
Karamar hukumar Mafara an samu labarin hare-haren a Tabkin Rama, Matsafa, da Ruwan Gizo, yayin da Rafin Jema a Gummi da Adabka da masu a Bukkuyum.
Kungiyar Zamfara Circle Community Initiative ta lura da cewa ci gaba da kai hare-hare na nuni da cewa akwai bukatar a dauki matakan tsaro cikin gaggawa domin kare al’umomin da ke karkara daga hare-haren ‘yan bindiga.



