DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jihohin Arewa 4 ne kawai ke biyan ‘yan fansho mafi karancin albashin N32,000 – kungiyar ‘yan fansho

-

Kungiyar ‘yan fansho ta Nijeriya NUP ta ce jihohi hudu ne kacal cikin 19 na jihohin Arewa suka bi umarnin gwamnatin tarayya na biyan ₦32,000 mafi karancin albashi na wata-wata.

Da yake jawabi Yayin taron shiyyar da ya gudana a jihar Kaduna, shugaban NUP, Kwamared Mohammed Sali, ya bayyana lamarin a matsayin Rashin adalci ga tsofaffi da suka sadaukar da shekaru da dama na yi wa kasa hidima.

Google search engine

Ya ce jihohi hudu ne kawai ke biyan mafi karancin ₦32,000 daga cikin 19 a duk wata.

A cewarsa jihohi da dama har Yanzu suna biyan kasa da ₦3,000, ₦4,000, ko ₦5,000,kuma wannan ba daidai ba ne indai ba so ake a gansu akan titi suna yawo ba.

Sakataren kungiyar Alhassan Balarabe Musa, ya kuma yi Allah-wadai da banbance-banbance tsakanin kudaden fansho na ‘yan fansho da wanda ‘yan siyasa ke samu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara