Shugaban Amurka, Donald Trump, ya umarci a gaggauta korar marasa matsuguni daga birnin Washington DC, yana mai cewa za a samar musu da wuraren zama amma nesa da babban birnin.
A wani saƙo da ya wallafa a Truth Social tare da hotunan tantuna da tarkacen da ke gefen titi, Trump ya ce masu aikata laifi za a tura su gidan yari.
Rahoton gidan talabijin na Channels ya ambato shi na bayyana cewa birnin zai zama mafi tsaro da tsabta fiye da da, kuma ya soki magajin garin birnin, Muriel Bowser.
Rahotanni sun nuna cewa gwamnatin tarayya na shirin tura sojojin National Guard don aiwatar da wannan umarni, duk da cewa ba a yanke hukunci na ƙarshe ba.
Kwanaki biyu da suka gabata, Trump ya bayyana cewa zai dauki mataki kan marasa matsuguni da ke kusa da Fadar White House.



