DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wata fasinja ta wanke ma’aikatan jirgin Ibom Air da mari a cikin jirgi

-

Hukumar gudanarwar Ibom Air ta ce wata mata mai suna Comfort Emmanson ta tada rikici a jirgin da ya taso daga Uyo zuwa Legas bayan ta ki kashe wayarta duk da umarnin da ma’aikatan jirgi suka yi.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, bayan jirgi ya sauka a Legas, ta kai wa Purser hari, ta taka kafafunta, sannan ta yi amfani da kwalbar kashe wuta a matsayin makami, ta kuma mari jami’an tsaro har ma da manajan filin jirgi.

Google search engine

Tuni dai Jami’an hukumar kula da harkokin Jiragen saman Nijeriya FAAN suka kama ta suka mika wa ‘yan sanda.

Kodaidai Kamfanin jirgin ya ce an haramta mata hawa duk wani jirginsu kuma sun mika rahoto ga NCAA, tare da jaddada manufarsu ta rashin lamuntar duk wani tashin hankali a jirginsu nan gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara