DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Har yanzu gwamnatin Nijeriya tana biyan tallafin man fetur a boye – Babachir Lawal

-

Tsohon sakataren gwamnatin Najeriya Babachir David Lawal ya caccaki gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, yana cewa ba zai iya aiki da ita ba, kuma da ya samu mukami da tuni ya yi murabus.

A hirarsa da gidan talabijin na Channels, Babachir ya zargi gwamnatin da nuna son kai da yawan baiwa ’yan kabilar Yarbawa mukamai, wanda hakan a cewar sa rashin adalci ne.

Google search engine

Ya kuma yi korafi kan manufofin tattalin arziki, musamman cire tallafin man fetur tun watan Mayun 2023, tare da cewa har yanzu ana biyan tallafin man fetur a boye, kuma ’yan Najeriya ba sa amfana da cirewar da aka yi.

Lawal ya ce tsarin mulkin Tinubu ya yi tasiri wajen haifar da hauhawar farashi da wahala ga talakawa a Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara