DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu a Abuja ta nemi a kawo karshen tuhumar da ake yi wa kanal Dasuki cikin kwanaki 45

-

Wata Babbar kotun tarayya a Abuja ta sanya ranakun 24, 25 da 26 ga watan Satumba don gwamnatin tarayya ta kammala shari’ar tsohon mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Kanal Sambo Dasuki game da tuhumar mallakar makamai ba bisa ka’ida ba da kuma almundahanar kudi.

Rahoton jaridar Daily Trust ya ce mai shari’a Peter Lifu ne ya bayar da wannan umarnin, bayan ya amince da bukatar gwamnati ta dage zaman don kawo karin shaidu, tare da bai wa wanda ake tuhuma damar kare kansa.

Google search engine

Shaida daga hukumar tsaron na farin kaya DSS Monsur Mohammed, ya tabbatar da cewa sun gudanar da bincike a gidajen Dasuki a biranen Abuja, Kaduna da Sokoto, inda suka samu makamai da wasu kayayyaki ciki har da kwamfuta, wayoyi, da takardun banki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara