Sufeto Janar na ’Yan Sandan Nijeriya, Kayode Egbetokun, ya kara wa’adin fara hukunta masu amfani da gilashin mota mai duhu ba tare da lasisi ba har zuwa 2 ga Oktoba.
Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito mai magana da yawun ’yan sanda na kasa, DCP Olumuyiwa Adejobi na cewa karin lokacin ya biyo bayan yawaitar neman lasisin ta shafin yanar gizo na hukumar, wanda ke nuna karuwar bin doka daga jama’a.
Ya bayyana cewa karin wa’adin zai bai wa hukumomi damar tantance masu nema sosai, da kuma ci gaba da inganta tsarin tantancewa na yanar gizo da na zahiri, domin tabbatar da sahihancin lasisin da kuma hana kaucewa ka’ida.



