DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tattalin arzikin Nijeriya na samun tagomashi a idon duniya -Minista Muhammad Idris

-

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a a Nijeriya, Mohammed Idris Malagi ya ce tattalin arzikin Najeriya yana samun habbaka da yabo daga manyan cibiyoyin kimanta tattalin arziki na duniya, abin da ke nuna ƙarin amincewa da alkiblar tattalin arzikin ƙasar.

Ya bayyana haka ne bayan ganawa da Gwamnan Imo kuma Shugaban Kungiyar Gwamnonin APC, Hope Uzodimma, a Abuja.

Google search engine

Muhammad Idris ya ce tsare-tsaren tattalin arzikin na shugaba Bola Tinubu sun fara haifar da sakamako mai kyau, inda rahotanni daga hukumomin ƙasa da ƙasa ke nuna kyakkyawan ci gaba a gyaran tattalin arziki da aiwatar da manufofin gwamnati.

Rahoton Daily Nigerian ya Ambato ministan na cewa, duk da cewa ba a kai ƙarshe ba, an riga an kafa hanyar da za ta kai ga cimma manufofin gwamnati, kuma kafin Tinubu ya kammala wa’adin mulkinsa na farko, fa’idodin waɗannan gyare-gyare za su bayyana ga ‘yan ƙasa.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara