DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Tinubu ta sa takunkumin kafa sabbin makarantun gaba da sakandare a Nijeriya har nan da shekaru 7 masu zuwa

-

Gwamnatin Nijeriya ta sanya wa’adin dakatar da kafa sabbin jami’o’i, kwalejojin fasaha da na ilimi na tarayya na tsawon shekaru bakwai, bisa hujjar yawaitar cibiyoyin da ake amfani da su kasa da yadda ya kamata, karancin albarkatun da ake da su, da kuma raguwar ingancin ilimi.

An amince da wannan matakin ne a zaman Majalisar Zartarwa ta Tarayya da aka gudanar ranar Laraba a fadar shugaban kasa, Abuja, karkashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, bayan gabatarwar da Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ya yi.

Google search engine

Sai dai, duk da wannan takunkumi, Majalisar ta amince da kafa sabbin jami’o’i tara.

Da yake zantawa da ’yan jarida a fadar shugaban ƙasa bayan zaman, Alausa ya ce matsalar tsarin ilimi na manyan makarantu a Najeriya yanzu ba samun gurbi ba ce, sai dai yawaitar maimaita cibiyoyi marasa amfani yadda ya dace, ƙarancin gine-gine, rashin isassun malamai, da kuma raguwa a yawan ɗaliban da ke shiga a yawancin cibiyoyin da ake da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara