DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Tinubu ta sa takunkumin kafa sabbin makarantun gaba da sakandare a Nijeriya har nan da shekaru 7 masu zuwa

-

Gwamnatin Nijeriya ta sanya wa’adin dakatar da kafa sabbin jami’o’i, kwalejojin fasaha da na ilimi na tarayya na tsawon shekaru bakwai, bisa hujjar yawaitar cibiyoyin da ake amfani da su kasa da yadda ya kamata, karancin albarkatun da ake da su, da kuma raguwar ingancin ilimi.

An amince da wannan matakin ne a zaman Majalisar Zartarwa ta Tarayya da aka gudanar ranar Laraba a fadar shugaban kasa, Abuja, karkashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, bayan gabatarwar da Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ya yi.

Google search engine

Sai dai, duk da wannan takunkumi, Majalisar ta amince da kafa sabbin jami’o’i tara.

Da yake zantawa da ’yan jarida a fadar shugaban ƙasa bayan zaman, Alausa ya ce matsalar tsarin ilimi na manyan makarantu a Najeriya yanzu ba samun gurbi ba ce, sai dai yawaitar maimaita cibiyoyi marasa amfani yadda ya dace, ƙarancin gine-gine, rashin isassun malamai, da kuma raguwa a yawan ɗaliban da ke shiga a yawancin cibiyoyin da ake da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara