DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilai na shirin yin kudirin sanya kotun daukaka kara ta zama matakin karshe a shari’o’in zaben gwamna Wani dan Majalisar Wakilai, Bayo Balogun, ya ce majalisar tana aiki kan kudirin gyara kundin tsarin mulki na 1999 domin sanya Kotun Daukaka Kara ta zama matakin karshe a shari’o’in zaben gwamna, ba tare da kai kara zuwa Kotun Koli ba. Balogun, wanda shi ne shugaban kwamitin INEC a majalisar, ya bayyana hakan a shirin Politics Today na Channels TV, inda ya ce kudirin zai rage lokacin sauraron karar zabe daga kwana 90 a kotun farko zuwa kwana 50 a matakin daukaka kara, tare da takaita lokacin gabatar da kara da daukaka kara. Ya kara da cewa, idan aka amince da kudirin, INEC za ta gudanar da zabukan gwamna da wuri don kammala shari’o’in zabe kafin karewar wa’adin gwamnoni, kuma za a rage matakan sauraron kara daga uku zuwa biyu kacal.

-

Majalisar wakilai na shirin yin kudirin sanya kotun daukaka kara ta zama matakin karshe a shari’o’in zaben gwamna

Wani dan Majalisar Wakilai, Bayo Balogun, ya ce majalisar tana aiki kan kudirin gyara kundin tsarin mulki na 1999 domin sanya Kotun Daukaka Kara ta zama matakin karshe a shari’o’in zaben gwamna, ba tare da kai kara zuwa Kotun Koli ba.

Google search engine

Balogun, wanda shi ne shugaban kwamitin INEC a majalisar, ya bayyana hakan a shirin Politics Today na Channels TV, inda ya ce kudirin zai rage lokacin sauraron karar zabe daga kwana 90 a kotun farko zuwa kwana 50 a matakin daukaka kara, tare da takaita lokacin gabatar da kara da daukaka kara.

Ya kara da cewa, idan aka amince da kudirin, INEC za ta gudanar da zabukan gwamna da wuri don kammala shari’o’in zabe kafin karewar wa’adin gwamnoni, kuma za a rage matakan sauraron kara daga uku zuwa biyu kacal.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara