DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rashin isassun kudi ya sa gwamnatin Najeriya fara lalubo hanyoyin cefanar da tashar jiragen ruwa ta Baro da ke Jihar Neja

-

Ministan da ke kula da harkokin tattalin arzikin teku a Najeriya, Adegboyega Oyetola, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya na shirin cefanar da tashar jiragen ruwa ta Baro da ke Jihar Neja ga ‘yan kasuwa, domin farfaɗo da ita.

Ya bayyana hakan ne a gaban kwamitin wucin gadi na majalisar wakilai da ke nazarin kalubale da damar farfado da tashar, inda ya ce tun bayan kaddamar da ita a 2019 ba ta yi aiki yadda ya kamata ba saboda rashin hanyoyin mota, layin dogo da matsalar zurfin ruwa.

Google search engine

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito Oyetola ya ce akwai buƙatar sake zurfafa kogin da haɗa tashar da hanyoyi jirgin kasa, amma rashin kuɗi ya takaita aikin.

Ya bayyana cewa gwamnati na aiki tare da ma’aikatun ayyuka da sufuri, tare da shirin jawo hankalin masu zuba jari na musamman domin cefanar da ita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara