Hedikwatar tsaron Nijeriya ta musanta rahotannin da ke cewa dan bindiga Bello Turji ya mika wuya ga sojoji.
Daraktan yada labarai na hedikwatar tsaron, Manjo Janar Markus Kangyebya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja yayin wani taron manema labarai kan ayyukan rundunar.
Bello Turji, wanda ake nema ruwa a jallo, na gudanar da ayyukan sa na ta’addanci ne musamman a jihohin Zamfara da Sokoto, kuma ana zarginsa da kai hare-hare da dama a yankin Arewa maso yamma.
A kwanakin baya wasu rahotanni sun ce Turji ya ajiye makamansa tare da sakin mutane 32 da aka yi garkuwa da su, bayan wani shirin sulhu da malamai suka jagoranta a Zamfara.
Hedikwatar tsaron ta ce har yanzu babu wani tabbaci kan wannan ikirari.



