DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya tashi daga Abuja a ziyarar da zai kai kasashen Japan da Brazil

-

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya bar Abuja zuwa kasashen Japan da Brazil domin halartar taro da kuma ziyarar aiki.

A cewar mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga, Tinubu zai fara tsayawa a Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa kafin ya wuce Japan.

Google search engine

Shugaban kasar zai halarci taron kasa da kasa karo na 9 kan cigaban Afirka (TICAD9) a birnin Yokohama daga ranar 20 zuwa 22 ga watan Agusta, za a gudanar da taron ne domin tattauna batutuwan cigaban Afirka, inda Tinubu zai shiga zaman tattaunawar kuma zai gana da shugabannin kamfanoni masu zuba jari daga Japan a Najeriya.

Bayan kammala taron, shugaban Najeriya zai wuce Brazil daga ranar Lahadi 24 zuwa Litinin 25 ga watan Agusta, bisa gayyatar shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara