DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mutane 62 da aka sace sun kubuta bayan luguden wuta kan sansanin yan bindiga a Katsina

-

Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da cewa mutum 62 da aka yi garkuwa da su sun kubuta, biyo bayan luguden wuta da rundunar sojin sama ta kai a sansanin fitaccen jagoran yan bindiga Muhammadu Fulani, a karamar hukumar Dan-Musa.

Kwamishinan tsaro na cikin gida Dr Nasir Mu’azu ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa luguden wutar sojin saman ya kai ga yankin Jigawa Sawai, da ke kan iyakar Katsina da Zamfara

Dr Nasir Mu’azu yace daga cikin mutanen da suka kubuta, mutum 12 suna samun kulawar likitoci a Asibitin Gwamnati dake Matazu, yayin da wasu 16 ke tare da sojojin Najeriya a Kaiga Malamai.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tinubu ya gargadi Alkalan Nijeriya da kada su karkata ga cin hanci ko rashin adalci

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga alkalai da sauran ma’aikatan shari’a a Najeriya da su ci gaba da zama masu gaskiya, adalci,...

PDP ta musanta zargin kirƙirar sa hannun Sakataren ta na kasa

Kwamitin zartaswa na Ƙasa na jam’iyyar PDP ya musanta zargin ƙirƙirar sa hannu da Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, ya yi. Mai magana da...

Mafi Shahara