DCL Hausa Radio
Kaitsaye

ADC ta yi watsi da batun ƙarin albashin shugaban ƙasa, gwamnoni da sauran manyan jami’an gwamnati a Nijeriya

-

Jam’iyyar ADC ta bayyana adawa da shirin ƙarin albashi ga masu rike da mukaman siyasa da hukumar RMAFC ta gabatar.

Jam’iyyar ta ce wannan mataki abin tozarci ne ga talakawan Nijeriya da ke fama da tsadar rayuwa, hauhawar farashin kayayyaki, da rashin ingantaccen tsarin albashi.

Google search engine

A cikin sanarwar da mai magana da yawun jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar, ADC ta ce albashin da ake bai wa manyan jami’an gwamnati da alawus- alawus ya zarce misali idan aka kwatanta da abinda talakawa ke samu.

Jam’iyyar ta jaddada cewa maimakon ƙarin albashi ga shugabanni, ya fi dacewa a mayar da hankali kan ƙara mafi ƙarancin albashi, tabbatar da biyan ma’aikata akan lokaci don rage wahalar da al’umma ke cike.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara