Kotun Jihar Filato mai lamba 7 ta bayar da belin mutane 20 da ake zargi da hannu a halaka mutane 13 da suka halarci biki a kauyen Mangun, karamar hukumar Mangu na jihar.
An ba da belin ne a ranar Alhamis, inda mai shari’a Nafisa Lawal Musa ta saurari roƙon lauyan wadanda ake tuhuma, Barista Garba Pwul SAN.
An gano cewa wadanda abin ya faru da su, an halaka su ne a ranar 12 ga Yuni, 2025, yayin da suke hanyarsu domin halartar daurin auren dan uwansu.
‘Yan sanda sun gurfanar da mutanen 20 a gaban kotu bisa tuhume-tuhume guda hudu da suka haɗa da, hada baki wajen aikata laifi, amfani da makamai masu hatsari, halaka wasu da kuma jikkata mutane da gangan.
Tun da farko, a watan Yuli, lauyoyin da ke kare wadanda ake tuhumar sun nemi kotu ta ba su beli amma ba su samu ba saboda kotun ta shiga hutu,hakan ya sa aka dage sauraren shari’ar zuwa ranar 13 ga Oktoba, 2025.
Sai dai a ranar 14 ga Agusta, 2025, mai shari’a Musa ya amince da bukatar belin bayan karɓar ƙarar da aka gabatar a ranar 11 ga Agusta daga lauyan mutanen da ake tuhuma.



