DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna bukatar agajin gaggawa daga gwamnatin tarayya kan batun tsaro – Gwamnatin jihar Katsina

-

Mukaddashin Gwamnan Jihar Katsina, Farouk Lawal Jobe, ya roƙi Shugaba Bola Tinubu ya gaggauta ɗaukar matakai na musamman wajen kawo ƙarshen hare-haren ’yan bindiga da suka ƙara ta’azzara a jihar.

Wannan roƙo na zuwa ne bayan wani mummunar harin da aka kai wa al’ummar Mantau, karamar hukumar Malumfashi, inda ’yan bindiga suka kashe mutane 13 a masallaci yayin da suke salla da safiyar Talata.

Google search engine

A cewar Jobe, hare-haren sun fi yawa musamman a lokacin damina, abin da ke bai wa ’yan ta’adda damar fakewa cikin dazuzzuka suna kai farmaki kan manoma da mazauna yankunan.

Ya ce akwai buƙatar Shugaban Ƙasa ya ba hukumomin tsaro umarnin kai tsaye domin kawo ƙarshen wannan barazana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara