DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin PDP za su yi taro a Zamfara kafin babban taronsu na kasa

-

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, zai karɓi baƙuncin sauran gwamnoni na jam’iyyar PDP a Gusau ranar Asabar, 23 ga watan Agusta, 2025.

Wannan taro dai na musamman ne da aka shirya domin tsara dabarun jam’iyyar tare da shiryawa babban taron kasa da za a gudanar a Ibadan, jihar Oyo, ranar 15 zuwa 16 ga watan Nuwamba, 2025.

Google search engine

A cewar sanarwar da mai magana da yawun Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, taron zai zama wata dama ta tattaunawa kan manyan batutuwan siyasa, ƙarfafa haɗin kai a cikin jam’iyyar, da kuma haɗa kai wajen ci gaban jihohin da gwamnoni ke jagoranta.

An bayyana cewa gwamnoni za su isa Gusau tun da yammacin Juma’a, inda Gwamna Dauda zai shirya musu liyafa kafin zaman da zasu gudanar a ranar Asabar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara