Jerin sunayen masu kuɗi na duniya da mujallar Forbes ta fitar a karon nan ya nuna cewa ‘yan Najeriya hudu ne suka samu shiga cikin manyan attajirai a duniya.
A sahun gaba akwai Alhaji Aliko Dangote, wanda aka kiyasta dukiyarsa ta kai dala biliyan 24.4, yana matsayin na 88 a duniya.
Wannan ya ba shi tazara sosai daga sauran ‘yan Najeriya a jerin.
A bayan sa akwai: Abdulsamad Rabiu mai dala biliyan 7.2 da ke mataki na 516, sai Mike Adenuga mai dala biliyan 6.3 da ke matsayi na 592, da kuma Femi Otedola mai dala biliyan 1.5 wanda ke matsayi na 2,424.
Bambancin dukiya tsakanin Dangote da sauran abokan kasuwancinsa ta ninka adadin ta su Abdussamad Rabiu sau uku, ta fi ta Adenuga sau huɗu, sannan ta fi ta Otedola sau 16, kamar yadda binciken jaridar ya tabbatar.



