DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Atiku yafi sha’awar gyaran Nijeriya fiye da burinsa na zama shugaban kasa

-

Wani na kusa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa Atiku ya fi sha’awar ganin Najeriya ta gyaru fiye da burin zama shugaban ƙasa.

Maganar ta fito ne yayin taron karɓar sabbin masu sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ADC da aka gudanar a Legas ranar Asabar.

Google search engine

A cewar rahoton Punch mai dogaro da NAN, wasu manyan jiga-jigan jam’iyyun PDP da Labour Party ne suka sauya sheƙa zuwa ADC.

A wajen taron, Farfesa Ola Olateju daga Jami’ar Achievers da ke Owo, Jihar Ondo, wanda ya wakilci Atiku a wurin gangamin, ya bayyana cewa Atiku “ba ya azarbabin sai ya zama shugaban ƙasa, amma yana da kishin ganin Najeriya ta samu tsaro, ci gaba da kuma wadata.”

Rahotanni sun ce Atiku, tare da wasu ’yan adawa masu ra’ayi irin nasa, sun fice daga jam’iyyar PDP zuwa ADC a shirye-shiryen fafatawa a zaben 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara