DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babban hafsan tsaro bai ce ‘yan kasa su ɗauki makamai ba

-

Hedikwatar tsaron Najeriya ta bayyana cewa maganar da shugaban rundunar tsaro Janar Christopher Musa, ya yi ba ya nufin kiran ‘yan ƙasa su ɗauki makamai su kare kansu.

Daraktan yaɗa labaran ma’aikatar tsaro ta kasa, Brig. Janar Tukur Gusau, ya ce an yi kuskuren fahimtar maganganun CDS da ya yi a hira da gidan talabijin na Channels a ranar Alhamis.

Google search engine

A cewarsa, Christopher Musa ya ƙarfafa ‘yan Najeriya ne su koyi dabarun kare kai da ɗaukar darussa irin su Taekwondo, Judo, Dambe, Iyo, da Tuƙi, ba wai yana kira su ɗauki makamai ba.

Ya kuma yi kira ga jama’a da su riƙa duba asalin tushen magana kafin yada ta, tare da jaddada cewa rundunar soji da sauran hukumomin tsaro na samun nasarori a yaƙi da rashin tsaro a fadin ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara