DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Katsina ta kashe Naira Biliyan 36 a harkar tsaro

-

Gwamnatin Malam Dikko Umar Radda ta bayyana cewa kimanin Naira biliyan 36 ta kashe a fannin tsaron jihar.

Kwamishinan tsaro cikin gida Dr Nasir Danmusa ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da ya gudana a gidan gwamnatin jihar jim kadan bayan kammala wani taron masu ruwa da tsaki a harkar tsaro.

Google search engine

A cewar gwamnatin yanzu jihar na da motocin sulke na APC guda 42 da wasu muhimman kayayyakin yaki domin kare al’ummar jihar daga yan fashin daji.

“Ko a safiyar Asabar dinnan mun ceto mutane 76 da aka yi garkuwa da su a dajin Fauwa” in ji Kwamishinan.

Kwamishinan ya kara da cewa yanzu jihar ta fara samun sauki daga hare-haren yan bindiga.

Jihar Katsina dai na daga cikin jihohin Arewa da ke fama da hare-hare yan bindiga, ko a satin da ya gabata an hallaka mutane sama da 27 a kauyen gidan mantau dake karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara