DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar sojin saman Nijeriya ta ceto mutane 76 daga hannun ’yan bindiga a Katsina

-

Dakarun sojojin sama na Najeriya NAF sun kai farmaki a kan mafakar fitaccen ɗan bindiga Babbaro a Tudun Pauwa, Karamar Hukumar Kankara, inda suka ceto mutane 76 da aka yi garkuwa da su, ciki har da mata da ƙananan yara.

A cewar Ma’aikatar tsaron cikin gida, sun dukkan mutanen da aka sace a lokacin harin da aka kai Unguwar Mantau da ke Malumfashi, sai dai an tabbatar da rasuwar yaro ɗaya a cikin lamarin.

Google search engine

Farmakin jiragen saman ya gudana tsakanin ƙarfe 6:00 zuwa 7:00 na yamma, inda aka kai hari kai tsaye kan mafakar danbindiga Babbaro, wacce ta dade tana zama barazana ga al’ummomin yankin.

Gwamnatin jihar Katsina ta jinjinawa dakarun hadin-gwiwar sojojin sama, sojin kasa da sauran hukumomin tsaro bisa ƙoƙarinsu, tare da jaddada cewa za ta ci gaba da bayar da goyon baya ta fuskar kayan aiki, bayanan leƙen asiri da haɗin gwiwar al’umma domin tabbatar da dorewar zaman lafiya a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara