DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Peter Obi na bukatar nazari don kada ya rasa damarsa a 2027 – Farfesa Adibe

-

Wani masani a fannin siyasa, Farfesa Jideofor Adibe, ya gargadi ɗan takarar shugaban ƙasa a zaben 2023, Peter Obi, da ya yi taka-tsantsan da jam’iyyar adawa ta ADC, domin kada ya rasa damar tsayawa takara a 2027.

Da yake magana a shirin The Morning Brief na gidan talabijin na Channels, Farfesa Adibe ya ce manyan jam’iyyun PDP da APC sun riga sun karkata tikitin shugabancin ƙasa zuwa kudu, yayin da ADC ba ta bayyana matsayinta ba tukuna.

Google search engine

Ya kuma nuna cewa tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, na nuna sha’awar tsayawa takara a 2027 a ƙarƙashin haɗakar ADC, abin da ka iya zama barazana ga ’yan kudu irin su Obi da Rotimi Amaechi.

Farfesa Adibe ya bayyana Obi a matsayin mutum mai zurfin tunani, amma ya jaddada cewa dole ne ya yi taka-tsantsan da shiri, yana kwatanta halin siyasar Najeriya da wasan catur wanda komai zai iya sauyawa a kowanne lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara