DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun sace magidanci tare da iyalansa a tsakiyar garin Katsina

-

Yan bindiga dauke da makamai sun shiga cikin garin Katsina a daren ranar Litinin a wata unguwa Filin Kanada sabuwar unguwar Kofar kaura dake tsakiyar birnin jihar.

Makwabcin wanda iftila’in ya shafa, ya kuma bukaci a sakaya sunansa, ya shaida ma DCL Hausa yadda lamarin ya faru.

Google search engine

A cewar sa, wasu da ake zargin yan fashin daji ne sun sace makwabcin sa mai suna Anas Ahmed da maidakinsa Halimatu da kuma diyarsu.

Maharan sun ziyar ci unguwar da misalin karfe 3:00 na dare kuma sun hallaka wani danbanga nan take, wanda yake aikin tabbatar da tsaro a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yadda na rasa É—iyata da jikokina sanadiyyar shan ‘Dettol’ a matsayin magani

Rashin sani ya haddasa mutuwar yata da jikokina bayan da suka sha Dettol a matsayin magani Wata dattijuwa mai suna Asiya Hassan da ke zaune a...

Shugaban Sashen Hausa na BBC Aliyu Tanko ya ajiye aiki

Shugaban Sashen Hausa na BBC, Aliyu Abdullahi Tanko, ya ajiye aikinsa bayan ya shafe shekaru 17 yana aiki da gidan. Tanko, wanda ya zama babban...

Mafi Shahara