DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mun dauki alhakin faduwar jirgin fasinjan Kaduna zuwa Abuja – Hukumar NRC

-

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Nijeriya (NRC), Kayode Opeifa, ya bayyana cewa ya ɗauki cikakken alhakin hatsarin da ya rutsa da jirgin fasinjan Abuja zuwa Kaduna a ranar Talata.

Shugaban ya ce hatsarin bai yi sanadiyyar mutuwar wani ba, abin da ya kira “rufin asirin Allah” domin irin wannan haɗari kan munana a wasu lokutan.

Google search engine

Duk da haka, ya tabbatar da cewa mutane huɗu daga cikin fasinjoji sun samu mummunan rauni, yayin da wasu biyu aka sallame su daga asibiti nan take.

Opeifa ya bayyana cewa hatsarin bai kamata ya faru ba, kuma NRC za ta tabbatar da cewa irin haka ba zai sake faruwa ba.

A yayin tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, ya ce Yanzu haka sun dakatar da hanyar Warri-Itakpe makonni uku da suka gabata saboda tsaro, inda ake yin gyaran manyan layin jirgin domin gujewa irin wannan matsala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara