DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mun dauki alhakin faduwar jirgin fasinjan Kaduna zuwa Abuja – Hukumar NRC

-

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Nijeriya (NRC), Kayode Opeifa, ya bayyana cewa ya ɗauki cikakken alhakin hatsarin da ya rutsa da jirgin fasinjan Abuja zuwa Kaduna a ranar Talata.

Shugaban ya ce hatsarin bai yi sanadiyyar mutuwar wani ba, abin da ya kira “rufin asirin Allah” domin irin wannan haɗari kan munana a wasu lokutan.

Google search engine

Duk da haka, ya tabbatar da cewa mutane huɗu daga cikin fasinjoji sun samu mummunan rauni, yayin da wasu biyu aka sallame su daga asibiti nan take.

Opeifa ya bayyana cewa hatsarin bai kamata ya faru ba, kuma NRC za ta tabbatar da cewa irin haka ba zai sake faruwa ba.

A yayin tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, ya ce Yanzu haka sun dakatar da hanyar Warri-Itakpe makonni uku da suka gabata saboda tsaro, inda ake yin gyaran manyan layin jirgin domin gujewa irin wannan matsala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara