DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ziyarar Tinubu a Brazil kofar samun hannun jari ce ga Nijeriya – Uba Sani

-

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce ziyarar aiki da Shugaba Bola Tinubu ya kai ƙasar Brazil na iya buɗe kofofin zuba jari sama da dala biliyan 30 a sassan tattalin arzikin Najeriya.

Da yake jawabi ga manema labarai a Brasília, Sani ya bayyana cewa yarjejeniyoyin da aka cimma a fannoni kamar noma, samar da abinci, jiragen sama da fasaha, za su iya sauya yanayin tattalin arzikin ƙasar.

Google search engine

Ya kuma ambaci sabbin yarjejeniyoyi a bangaren diflomasiyya, kirkire-kirkire da makamashi, yana mai cewa matakan da Tinubu ya ɗauka, musamman cike gibin dala biliyan 7 na canjin kuɗi, sun dawo da amincewar masu zuba jari ga kasar.

Gwamnan ya jaddada cewa goyon bayan ‘yan Najeriya ga shirin tattalin arzikin gwamnatin Tinubu zai taimaka wa kasar ta tsaya da kafafunta kamar yadda jaridar Daily Nigerian ta tattaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara