DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jonathan ya ja girmansa, kada Tinubu a 2027 ba abu ne mai yuwuwa ba – APC

-

Jam’iyyar APC reshen Jihar Legas ta bayyana cewa duk da girma da darajar tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, ba shi da karfin siyasa da zai iya kayar da Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

Jam’iyyar ta yi wannan bayani ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta, Seye Oladejo, ya fitar ranar Juma’a, inda ya mayar da martani kan jita-jitar da ke cewa Jonathan na iya tsayawa takarar shugaban kasa a 2027.

Google search engine

Rahoton jaridar Daily Nigerian ya ambato Mr. Oladejo ya ce kalubalen da ake fuskanta a yau da gobe na bukatar shugabanci mai ƙarfin hali da hangen nesa, ba wai komawa ga abin da ya kira jiran gawon shanu ba.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara