DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu zai magance matsalolin Najeriya kafin ya sauka a mulki – Hon. Abejide

-

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabun Yagba Gabas, Yagba Yamma da Mopamuro, Leke Abejide, ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai wuce tsammanin jama’a tare da magance matsalolin kasar kafin karshen wa’adinsa.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa Abejide ya yi wannan bayani ne lokacin da ya karɓi tawagar Renewed Hope Ambassadors a ofishinsa ranar Laraba.

Google search engine

Tawagar ta samu jagorancin Abbas Mustapha, Koodinetan Kasa, da kuma Mustapha Alfa Makanta, Sakatarenta na Kasa.

Kungiyar ta bayyana cewa ziyarar ta zama wani bangare na tuntuba da tattaunawa da shugabanni da suka nuna goyon baya ga manufofin gwamnatin shugaba Tinubu.

Haka kuma sun jaddada cewa duk da kasancewarsa dan jam’iyyar ADC, Abejide ya nuna bajinta wajen fifita ci gaban kasa a kan banbancin jam’iyya, tare da mara wa manufofin Tinubu baya domin tabbatar da sauyi na gari a Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara