DCL Hausa Radio
Kaitsaye

NAHCON ta gargadi maniyyata Hajjin 2026 na Nijeriya kan yin rijista da wuri

-

By Fatima Aminu Dabo

Hukumar jin daɗin alhazai ta kasa NAHCON ta sanar da jadawalin aikin Hajjin 2026, inda ta bayyana cewa 20 ga Maris, 2026 ce ƙarshe wajen fitar da visa, tare da jaddada cewa ba za a yi ƙarin lokaci ba.

A cikin sanarwar da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ta ce za a rattaba hannu kan yarjejeniyar shirye-shirye da hukumomin Saudiyya a watan Nuwamba, 2025, yayin da ta sanya 8 ga Oktoba, 2025 a matsayin rana ta ƙarshe ta tura kuɗaɗen jihohi da masu gudanar da hajji domin tabbatar da gurabe.

NAHCON ta yi kira ga hukumomin jihohi da kamfanonin jigilar mahajjata da su bi wannan jadawali don guje wa matsaloli, tare da tabbatar da hajji mai tsari da kwanciyar hankali ga ’yan Najeriya.

Google search engine

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara